Innalillahi Kalli Yadda Wata Budurwa ta budewa Malamin ta gaban ta yana kallah

Innalillahi Kalli Yadda Wata Budurwa ta gudawa Malamin ta gaban ta yana kallah
NASIHA GA YANMATA DA ZAWARAWA, MUSAMMAN MA GA YANMATA !
Ki kiyayi shan abin kara kiɓa domin yana kokarin zamo wa abin zargi a yau, ke da kika kasance nutsassiya, kiyi hakuri ko kina sha ki daina ki godewa ALLAH a matsayin da ya yi ki, in ba haka ba za ki ja wa kanki babban matsala musamman ta fuskar mutunci da kuma auruwa

Akwai yanmata da ba nutsassu ba sukanje su sha magani ko sanya abin hana É—aukar ciki robar hannu, to wai yana sanya wasu jiki, shine sai yarinya tayi jiki ayi ta mamakin me ya sanya ta jiki, ko ayi ta cewa magani tasha ashe ashe …… Abinda yake gaskiyar magana biye biyen maza take wanda daman duk mace yarinya BUDURWA da take bin maza yanayin ta na sauyawa sosai to ga kuma in tayi planning yazo planning din tana daga cikin wa’enda yake sanyawa jiki.

Babban jan hankali ga yanmata masu irin wannan halin su ji tsoron ALLAH suna tuna mutuwa, yanzu har zamani ya kai yarinya ta zamo har da planning, ? Wannan musiba ce.

Abu na biyu yanmata wa’enda su ba aikata aikin banza suke ba ku ji tsoron ALLAH ku rufawa kanku asiri, in ba ki sha kada ki sha, in kina sha kidaina don yana da illa sosai ga lafiya, sa’annan kuma yanzu magana ta canja salo ke watakila ba ki daga cikin yanmata masu ÆŠabi’ar yawon banza, maganin kiÉ“a kika sha azo ana zargin ki, ana bata miki suna.



Daga karshe ina jan hankali ga iyaye, yayyu, da yan uwa musulmi mu ji tsoron ALLAH muna kulawa da amanar ya’yan mu da kannai, da yan’uwa musulmi.

Maza kuma aji tsoron ALLAH, a daina shigar da ya’yan mutane harkar banza don wata sanadin lalacewarta daga yaudara ce, ku kuma mata adaina kwaÉ—ayi da É—aukar wa kai Rayuwa ta karya, a kame kai a fuskanci abinda zai amfanar da rayuwa a cire kwaÉ—ayi da buri ayi aure, sai na canja waya ko sanya sutura da sauran kwaÉ—ayi shi ke hallakar da mata, babu nutsuwa ko kwanciyar hankali da tunani mai kyau ga duk wanda ya auka irin Mummunar ÆŠabi’ar nan, irin wa’ennan matsalolin ne ke hanawa yanmata aure, daga anzo neman aure abubuwa su lalace, ki natsu tun farko kiji tsoron ALLAH sai ki kalli kin gama yanmatanci lafiya, kin karatu, jin koyi sana’a, kinsamu miji kin yi aure.

Post a Comment

0 Comments